Mutane 2 sun mutu a wajen gangamin kamfen din Buhari a Jalingo

Rahotanni sun kawo cewa mutane biyu sun rasa ransu a ranar Alhamis, 7 ga watan Fabrairu
lokacin gangamin kamfen din Shugaban kasa Muhammadu Buhari a Jalingo, babbar birnin jihar Taraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa lamarin ya afku ne sanadiyar yawan mutanen da suka halarci wajen taron na Jolly Nyame. Dubban magoya bayan APC daga fadin kananan hukumomi 16 da ke jihar sun halarci taron kamfen din.

Karanta kaji wa yan BokoHaram sukeso yaci zaben gobe
Waye yan shi'a zasu zaba?

yakin neman zabe yakai wasu ga halaka



 Mutane 2 sun mutu a wajen gangamin kamfen din Buhari a Jalingo Source: UGC An tattaro cewa anyi gaggawan kai wadanda abun ya cika dasu cikin motocin asibiti da aka ajiye a wajen taron.
Hakazalika yawan jama’a ya dakatar da zirga-zirgan motoci na tsawon wasu sa’o’i a hanyar Jalingo-Yola. Shugaban kasa Buhari dai na neman zarcew ne a zaben ranar 16 ga watan Fabrairu.

Enregistrer un commentaire

Plus récente Plus ancienne