- Mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo, yayi hatsari a hanyarsa na daga Abuja zuwa Kabba da ke jihar Kogi
- Laolu Akande, mai magana da yawun Osinbajo, ya ce mataimakin shugaban kasan da tawagarsa suna nan lafia, kuma ba wanda yaji rauni.
- Osinbajo ya gana da Sarkin Kabba a jihar Kogi bayan wannan lamarin.
Kakakin 'yan sandan Osinbajo, Laolu Aknade, ya tabbatar da wannan lamarin, amma ya ce mataimakin shugaban ya kasance lafiya kuma ba a samu wani matsala ba.
Ya ce: Mataimakin Shugaban kasan, bayan iftila'in hatsarin jirgin saman(Helicopter), ya samu ya tsira da ranshi da sauran rundunanshi duka.
Kaman yanda ya sa a shafinshi ta Twitter.
