- Jam'iyyar PDP ta gargadi hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC akan soke zaben gwamna a jihar Bauchi
- Jihar Bauchi dai na daya daga cikin jihohin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana zabensu a matsayin zaben da bai kammala ba
- PDP ta ce ta samu wasu takardun bayanin sirri daga ofishin INEC na jihar Bauchi, kan yadda za su murde zaben jihar, wanda ya ce zasu fallasa nan ba da jimawa ba
Jam'iyyar PDP ta gargadi shuwagabannin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC da shugabanta, Farfesa Mahmood Yakubu, akan yin wasa ko murde sakamakon zaben kananan hukumomi 14 na jihar da aka rigaya aka sanar na zaben gwamnan jihar.
Haka zalika PDP ta yi gargadin cewa idan har aka yi duba da irin yanayin da jihar ta ke ciki na yadda siyasar ta dau zafi da kuma yadda kan masu kad'a kuri'a ya waye, duk wani yunkuri na sauya sakamakon zaben, zai iya haddasa babbar matsala a jihar.
Jihar Bauchi dai na daya daga cikin jihohin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana zabensu a matsayin zaben da bai kammala ba.
Tags
siyasa
