SABON SANARWA GAME DA KISAN JANAR IDRIS ALKALI

SABON SANARWA GAME DA KISAN JANAR IDRIS ALKALI



 Rundinar 'yan sandan Nigeria reshen jihar Pilato ta fitar da sabon sanarwa na neman wasu mutane 'yan kabilar berom mutum sha-uku (13) ana nemansu ruwa a jallo game da kisan Manjo Janar Idris Alkali



Cikin mutanen da rundinar 'yan sandan ta fitar da sanarwan nemansu ruwa a jallo mutum 13, 12 daga cikinsu sun fito daga kauyen Dwei ne dake gundumar Du, mutum 1 cikon na 13 ya fito daga kauyen Gushen a karamar hukumar Jos ta kudu

Ga sunayensu kamar haka:-
-Kannan Nyam 
-Solomon Gyang Jang
-Dustine
-Dung Deme
-Gyang Murrak
-Chuwang Samuel
-Nyam Samuel
-Dung Gbeh
-Daddy Dogo
-James Dung
-Gyang Dung
-Jay Boy

Maimagana da yawun rundinar 'yan sandan jihar Pilato DSP Mathias Tyopev yace; ayyana wadannan mutane da akayi a matsayin wadanda ake nema ruwa a jallo ya biyo bayan sabon bincike da rundinar 'yan sandan take cigaba da gudanarwa game da kisan Janar Idris Alkali, wanda hakan yasa ta gano suna da hannu dumu-dumu a ciki wajen kisan Janar din



Rundinar 'yan sanda reshen jihar Pilato tana rokon jama'a duk inda akaga wani mai suna irin na wadannan da aka lissafa a sama ayi kokarin kaiwa rahoto zuwa ofishin 'yan sanda mafi kusa, ko kuma a kira wadannan nambobin waya kamar haka: 07059473022, 08038907662, 08075391844, 09053872296.

Jama'a a taimaka wajen yada sanarwa.
Muna rokon Allah Ya tona musu asiri a duk inda suka buya a wannan duniyar

Allah Ka sa kisan Janar Idris Alkali yayi sanadin kawo karshen ta'addancin berom a kudancin Jos Amin
Allah Ka jikanshi Ka kyautata makwancinsa Amin


Enregistrer un commentaire

Plus récente Plus ancienne