An kama Malami Yana Lalata Da 'yar Shekara 18

Rundunar 'yan sanda a jihar Legas ta kama wani malamin makarantar sakandare da ake zargi da tilastawa daliban makarantar da yake koyarwa yin lalata da shi.

Ana zargin malamin da yin lalata da dalibarsa 'yar shekara 18 domin kara mata maki, bayan ta fadi jarrabawar da ta rubuta.

Babban jami'in yan sanda mai magana da yawun rundunar a jihar Legas, DSP Bala Elkanah ya tabbatar da kama malamin da ake zargi da sakawa dalibar 'yar shekara 18 da makin jarrabawa, bayan ya tilasta ma ta yin lalata shi da bakinta.

1 Commentaires

Plus récente Plus ancienne